Kwamitin BoT ta kuma tabbatar da korar dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar NNPP a zaben 2023, Sanata Rabi'u Musa Kwakwanso, rahoton Nigerian Tribune.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da aka fitar a karshen taron BoT na jam’iyyar NNPP wanda ya gudana a Otal din Rockview da ke Apapa, jihar Lagas a ranar Juma’a, 28 ga watan Satumba.
Jam'iyyar ta kuma bayyana cewa kundin tsarin mulkin jam'iyyar na 2022 zai ci gaba da kasance yadda yake cewa ba za a yi la'akari da gyara shi ba har sai bayan babban zaben 2027.
Sakataren labaran jam'iyyar na kasa, Alhaji Abdulsalam Abdulrasaq, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da aka gabatarwa manema labarai.
Published by isyaku.com