An gano jariri da wata mata ta sace a garin Minni jihar Neja, duba yadda ta faru


An gano wani jariri dan watanni shida mai suna Chinedu Chukwueke da wata mata ta gudu da shi a garin Minna na jihar Neja.

 A baya dai isyaku.com ya bayar da rahoton cewa matar ta sace jaririn ne bayan ta yi yaudarar cewa ita yar koyon aiki ce a shagon gyaran gashi salon na uwar yaron da ke Kure Ultra Modern Market, ranar Lahadi, 23 ga Yuli, 2023.

A wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Twitter a yammacin Laraba, mahaifin jaririn ya bayyana cewa an tsinci jaririn nasa ne a wani juji da ke kusa da ofishin 'yan sanda na Gauraka.  Ya ce an samu yaron nasa cikin koshin lafiya.

Published by isyaku.com
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN