Type Here to Get Search Results !

Main event

Ya Allah: An tsinci gawar wata mata a daji bayan an sace ta a Abuja


An tsinci gawar wata mata mai suna Maimuna Mohammed Sheke bayan an sace ta daga kauyen Yewuti da ke karamar hukumar Kwali a babban birnin tarayya Abuja.

 Wani mai Mai suna Usman Garba Fodio, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce an gano gawarta ne a wani daji da ke karamar hukumar Toto a jihar Nasarawa a ranar Talata, 16 ga Mayu, 2023.

 Wani ma’abocin amfani da Facebook, Abdul Jibrin Zubairu Yewuti shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin a wani sako da ya wallafa a Facebook.

 "Muna son ki amma Allah ya fi son ki.  Ya Maimuna Mohammed sheke, Allah ya sa ranki ya huta lafiya, aljanat firdaus ta zama makomarki ta karshe.

 Ku tuna cewa a baya ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu mutanen kauyen 29 a Yewuti.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies