Ya Allah: An tsinci gawar wata mata a daji bayan an sace ta a Abuja


An tsinci gawar wata mata mai suna Maimuna Mohammed Sheke bayan an sace ta daga kauyen Yewuti da ke karamar hukumar Kwali a babban birnin tarayya Abuja.

 Wani mai Mai suna Usman Garba Fodio, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya ce an gano gawarta ne a wani daji da ke karamar hukumar Toto a jihar Nasarawa a ranar Talata, 16 ga Mayu, 2023.

 Wani ma’abocin amfani da Facebook, Abdul Jibrin Zubairu Yewuti shi ma ya tabbatar da faruwar lamarin a wani sako da ya wallafa a Facebook.

 "Muna son ki amma Allah ya fi son ki.  Ya Maimuna Mohammed sheke, Allah ya sa ranki ya huta lafiya, aljanat firdaus ta zama makomarki ta karshe.

 Ku tuna cewa a baya ‘yan bindiga sun yi garkuwa da wasu mutanen kauyen 29 a Yewuti.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN