Type Here to Get Search Results !

Main event

Tashin hankali yayin da WHO ta ce annobar da ta fi COVID-19 na nan tafe


Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), ta gargadi mutanen duniya da su shirya wa wata annoba da ta fi cutar COVID-19 muni nan ba da jimawa ba.

Shugaban hukumar, Dokta Tedros Adhanom Ghebreyesus, ne ya bayyana hakan ranar Talata, yayin taron lafiya na duniya karo na 76 da yake gudana a birnin Geneva na kasar Switzerland. Jaridar Aminiya ta rahoto.

A cewarsa, “Akwai barazanar wata sabuwar nau’in cuta mai saurin yaduwa kuma mai saurin kisa, kuma har yanzu akwai barazanar cewa wannan cutar na iya bulla.

“Ba wai annobar cututtuka kawai muke fuskanta ba a duniyarmu yanzu haka. Shi kansa tsarin lafiya na duniya cikin tsananin bukata, kuma ya zama wajibi a tashi tsaye domin magance kalubalansa,” in ji shi.

Gargadin na zuwa ne ’yan makonni bayan Shugaban na WHO da kansa ya bayyana kawo karshen cutar ta COVID-19 a matsayin wata annobar ta duniya.

Sai dai ya ce babban taron na bana a kan lafiya wata babbar dama ce ga shugabanni a kowanne mataki su fito da nagartattun hanyoyi wajen magance su.

Bai dai bayyana sunan cutar ba, amma ya bukaci kowa da kowa da ya yi kyakkyawan shiri wajen yin maganinta a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN

Hollywood Movies