Madalla: An kama saurayi da ya caka wa mahaifiyarsa wuka har ta mutu a jihar Arewa


Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta cafke wani matashi dan shekara 22 mai suna Ibrahim Musa, wanda ya kashe mahaifiyarsa da wuka a karamar hukumar Nassarawa
.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, 5 ga watan Mayu, 2023, ya ce an kama wanda ake zargin ne a wata maboyar miyagun mutane da ke karamar hukumar Dawakin Tota a daren ranar Alhamis.

 A cewar PPRO, wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, sannan kuma ya amince da yin cinikin haramtattun kwayoyi.

 “A ranar 4 ga Mayu, 2023 da misalin karfe 2200 na rana, an kama Ibrahim Musa, ‘m’ mai shekaru 22 a wani maboyar masu laifi a karamar hukumar Dawakin Tofa, jihar Kano bayan ya daba wa mahaifiyarsa mai shekaru 50 wuka har lahira a karamar hukumar Nassarawa, jihar Kano.

 “Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa, sannan kuma ya amsa laifinsa na shan miyagun kwayoyi.  Za a gurfanar da shi gaban kotu bayan an kammala bincike.”

1 Comments

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN