Type Here to Get Search Results !

Madalla: An kama saurayi da ya caka wa mahaifiyarsa wuka har ta mutu a jihar Arewa


Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta cafke wani matashi dan shekara 22 mai suna Ibrahim Musa, wanda ya kashe mahaifiyarsa da wuka a karamar hukumar Nassarawa
.

 Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, 5 ga watan Mayu, 2023, ya ce an kama wanda ake zargin ne a wata maboyar miyagun mutane da ke karamar hukumar Dawakin Tota a daren ranar Alhamis.

 A cewar PPRO, wanda ake zargin ya amsa laifin da ake tuhumarsa da shi, sannan kuma ya amince da yin cinikin haramtattun kwayoyi.

 “A ranar 4 ga Mayu, 2023 da misalin karfe 2200 na rana, an kama Ibrahim Musa, ‘m’ mai shekaru 22 a wani maboyar masu laifi a karamar hukumar Dawakin Tofa, jihar Kano bayan ya daba wa mahaifiyarsa mai shekaru 50 wuka har lahira a karamar hukumar Nassarawa, jihar Kano.

 “Wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da aikatawa, sannan kuma ya amsa laifinsa na shan miyagun kwayoyi.  Za a gurfanar da shi gaban kotu bayan an kammala bincike.”

Post a Comment

1 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN