Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya kalubalanci magabatansa da su fito su rantse da Alkur’ani mai girma cewa ba su yi sata a asusun gwamnati ba a lokacin da suke kan mulki.
Gwamnan jihar Kaduna wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce a shirye yake ya yi hakan. PM News ta rahoto.
Yana mai mayar da martani ne a kan sukar da ya yi a ofis da daya daga cikin magabatansa, tsohon Gwamna Ahmed Makarfi.
A baya-bayan nan ne Makarfi ya yi korafin cewa gwamnatin El-Rufai ta bayar da sanarwar rusa wasu gine-ginen kamfanonin sa guda tara.
Sai dai El-Rufa’i, yayin da bai ambaci Makarfi kai tsaye ba, ya zargi wasu daga cikin magabatansa da yin amfani da kudaden da suka wawure lokacin da suke kan mulki wajen gina wasu gidaje a Kaduna da Dubai na Hadaddiyar Daular Larabawa.
Sabanin haka, shi Gwamnan mai barin gado ya ce bai saci kobo a baitul malin gwamnati ba tun lokacin da aka zabe shi ya hau mulkin Kaduna a 2015.
Ya ba da misali da cewa har yanzu yana da gida daya da ya gina kafin ya zama gwamna a Kaduna.
Ya ce hakan ya saba wa tsohon gwamnan da ba a bayyana sunansa ba, wanda ya yi amfani da kudaden da aka ce an sace a lokacin da ya ke kan mulki ya gina katafaren gida a titin Jabi a cikin tsohon birnin.
Gwamnan ya kuma yi alfahari da cewa ayyukan da ya fara za su dau shekaru masu yawa saboda ingancinsu
BY isyaku.com
RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI