Type Here to Get Search Results !

Matashiya ta haifi yara biyar, maza 3 mata 2, bayan shekara 8 bata haihu ba


Wata matashiya yar Najeriya wacce ta yi wa kasa hidima kwanan nan ta samu karuwar yara yan biyar.

Matar mai suna Chidimma Amaechi wacce ta fito daga jihar Ebonyi ta haifi yaran a Awka, babban birnin jihar Anambra. Legit Hausa ya wallafa.

A bisa wani labari da Okoye Ifeoma Obi, ya wallafa a Facebook, mai jegon ta haifi yaran shinkafa da wake wato maza uku da mata biyu.

Wannan gagarumin ni'ima da Chidimma ta samu yana zuwa ne bayan ta shafe shekaru takwas ba tare da haihuwa ba

Wani bangare na labarin ya ce:

"Mata na da karfi faaaaa. Yara biyar a lokaci daya. Ina rokon irin wannan, biyu kawai nake so. Wannan labari ne mai dadi da ya fito daga jihar Anambra. 

Ina taya Chidimma Amaechi wacce ta haifi yan biyar a Awka murnar wannan ni'ima na Ubangiji. Ta haifi maza 3 da mata 2 a asibitin Life Hospital Awka, jihar Anambra. Wannan ya cancanci ayi biki."

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN