Daliban Najeriya 4,000 sun makale sakamakon barkewar yaki a Sudan tsakanin bangarorin Janar 2 na soji, FG ta dau muhimmin mataki


Kimanin daliban Najeriya 4,000 ne ke makale a kasar Sudan sakamakon rikicin da ake fama da shi a can, in ji jaridar Daily Trust.

 Shugaban kungiyar daliban Najeriya, Sudan (NANSS), Abubakar Babangida, ne ya bayyana hakan ga jaridar Daily Trust.

 Hakan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da gwamnatin Najeriyar ta ce tana ci gaba da tuntuba mataki na gaba kan batun kwashe 'yan Najeriya a Sudan.

 Gwamnatin ta bayyana hakan ne a matsayin martani ga bukatar da daliban Najeriya a Sudan suka gabatar

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, an yi fama da tashin bama-bamai da harbe-harbe a babban birnin kasar Sudan a ranar Alhamis yayin da fadan da ake gwabzawa tsakanin dakarun janar-janar guda biyu bai nuna alamun raguwa ba gabanin bukukuwan karshen watan Ramadan.

 Sama da mutane 300 ne aka kashe tun bayan barkewar fadan a ranar Asabar tsakanin dakarun da ke biyayya ga Hafsan Sojin Sudan, Abdel Fattah al-Burhan da mataimakinsa, Mohamed Hamdan Daglo, wanda ke jagorantar runduna ta Rapid Support Forces (RSF).

 A zantawarsa da daya daga cikin ‘yan jarida a daren jiya, Babangida ya ce akwai dalibai ‘yan Najeriya sama da 10,000 da ke karatu a Sudan a halin yanzu.

 Sai dai ya ce galibin su suna hutu ne, inda ya ce kusan 4,000 daga cikinsu ne aka bari a baya.

 Ya ce daliban, galibinsu mata, sun makale ne a Sudan a halin yanzu.

Bayanai sun ce mahukuntan Najeriya na kokarin tsara yadda za ta kwashe sauran dalibai Yan Najeriya da suka makale a Sudan sakamakon barkewar fadan, musamman a Khartoum.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN