Rikici ya barke tsakanin wasu al'umma, an fille kan mutum daya, an kona gidaje, dukiya har amfanin gona


An sare kan mutum daya tare da lalata dukiyoyi na miliyoyin naira a wani sabon rikicin da ya barke tsakanin mutanen Oso-Edda da Amasiri a jihar Ebonyi.


 Oso-Edda yana cikin karamar hukumar Afikpo ta kudu yayinda Amasiri da Nde Ndukwe ke karamar hukumar Afikpo ta Arewa.


 A cewar jaridar Nigerian Tribune, al'ummomin sun shafe shekaru suna takaddama kan filaye a kan iyakokinsu amma an shawo kan lamarin tare da hana tashin hankali har zuwa wannan mako.


 Majiyoyi a yankin sun yi zargin cewa rikicin ya samo asali ne bayan da ‘yan kabilar Nde Ndukwe da Amasiri suka mamaye kauyukan da ke cikin Edda inda suka fara lalata gidaje da amfanin gona da duk wata kadarori da suka gani.


 An fara kai farmakin ne a ranar Litinin, 6 ga watan Fabrairu, kuma ya kai har zuwa Laraba lokacin da jami’an tsaro suka shiga domin dawo da zaman lafiya.


 An tattaro cewa maharan sun kashe wani mutum mai suna Chima Orji dan kabilar Idima mai cin gashin kansa a karamar hukumar Afikpo ta Kudu tare da sare masa kai.  Maharan sun dauke kai kuma har yanzu ba a gano su ba.


 Mafi muni shine kauyen Okporojo da ke Oso-Edda wanda aka ce an mayar da shi baraguzai da kango, an yi garkuwa da mutane hudu amma daga baya aka sako su bayan wani taron sulhu da shugabannin majalisun biyu suka shirya tare da wasu sarakuna da kuma shugaban tsaro.  Hukumomi a yankin.


 Shugaban karamar hukumar Afikpo ta Kudu, Chima Ekumankama, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa, ya bayyana lamarin a matsayin abin tausayi da raÉ—aÉ—i tare da yin kira ga daukacin dangin Edda da su kasance masu bin doka da oda.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN