Girgizar kasa da aka yi a kasar Siriya da Turkiyya ya yi sanadin mutuwar mutane 2,300

 


Kawo yanzu, rahotanni sun ce yawan wadanda suka mutu a girgizar kasar da ta auku a kasashen Turkiyya da Siriya ranar Litinin sun haura 2,300. Aminiya ta ruwaito.


Girgizar kasar wanda karfinta ya kai 7.8, ta lalata galibin biranen Turkiyya a yankunan da a nan galibin ’yan gudun hijira daga Siriya suke da zama.


Shugaban Cibiyar Kula da Girgizar Kasa na Kasar Siriya, Raed Ahmed, ya ce “Wannan ita girgizar kasa mafi karfin da cibiyar ta taba gani a tarihinta.”


An ga masu aikin ceto na ta kokarin bincike domin gano mutane da kasa ta rufta da su, walau a raye ko a mace.


Akalla mutum 810 aka ce sun mutu Siriya, sannan 1,498 a Turkiyya kamar yadda jami’au suka bayyana.


Kafin wannan lokaci, girgizar kasa mafi muni da Turkiyya ta gani ita ce wadda ta auku a 1939 inda mutum 33,000 suka mutu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN