Type Here to Get Search Results !

Da dumi-dumi: Saurayi ya rataye kanshi har Lahira a garin Argungu jihar Kebbi

 


Rahotanni daga garin Argungun a karamar hukumar Argungu jihar Kebbi na cewa ana zargin wani saurayi ya rataye kanshi har Lahira.

Shafin labarai na isyaku.com ya samo cewa lamarin ya faru ne ranar Lahadi 12/2/2023 da awannin tsakiyar rana.

An gano gawar yaron, (Mun sakaya sunansa) ana zargin dan kasa da shekara 20, ya rataye kanshi ne a wani bandaki da ke bayan dakin mahaifiyarsa a Unguwar Tudun wada a Birnin Argungu.

Bayanai na cewa za a yi jana'izarsa da karfe biyar na yammacin ranar Lahadi a garin Argungu.

Babu wani bayani kan musabbabin faruwar wannan lamari kawo yanzu.

Kakakin hukumar Yan sandan jihar Kebbi SP Nafiu Abubakar ya tabbatar da faruwar larin, ya ce " Mun sami rahotun faruwar lamarin" inji SP Nafiu.

Karin bayani na nan tafe...

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies