Da dumi-dumi: Saurayi ya rataye kanshi har Lahira a garin Argungu jihar Kebbi

 


Rahotanni daga garin Argungun a karamar hukumar Argungu jihar Kebbi na cewa ana zargin wani saurayi ya rataye kanshi har Lahira.

Shafin labarai na isyaku.com ya samo cewa lamarin ya faru ne ranar Lahadi 12/2/2023 da awannin tsakiyar rana.

An gano gawar yaron, (Mun sakaya sunansa) ana zargin dan kasa da shekara 20, ya rataye kanshi ne a wani bandaki da ke bayan dakin mahaifiyarsa a Unguwar Tudun wada a Birnin Argungu.

Bayanai na cewa za a yi jana'izarsa da karfe biyar na yammacin ranar Lahadi a garin Argungu.

Babu wani bayani kan musabbabin faruwar wannan lamari kawo yanzu.

Kakakin hukumar Yan sandan jihar Kebbi SP Nafiu Abubakar ya tabbatar da faruwar larin, ya ce " Mun sami rahotun faruwar lamarin" inji SP Nafiu.

Karin bayani na nan tafe...

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN