Ma’aikatan lafiya a Zamfara sun yi zanga-zangar rashin biyan albashi

Ma’aikatan lafiya a Zamfara sun yi zanga-zangar rashin biyan albashi


Kungiyoyin hadin gwiwa na bangaren lafiya na asibitin kwararru na Yariman Bakura da ke Gusau sun gudanar da zanga-zangar lumana a asibitin saboda rashin biyan albashi.

A baya dai kungiyar ta bayar da wa’adin mako guda ga gwamnatin jihar Zamfara da ta cire basussukan albashin ‘ya’yan kungiyar da kuma gyara rabin albashin da ake biyan wasu daga cikinsu.

Kungiyar ta bayyana cewa ta tuntubi hukumomin da abin ya shafa kan lamarin amma ba a yi komai ba duk da wasu tabbacin da aka bayar.

Sun ce gazawar hukumomin da abin ya shafa wajen aiwatar da bukatunsu cikin wa'adin sa'o'i 24 da suka gabata ya tilasta musu gudanar da zanga-zangar lumana.

An tattaro cewa baya ga asibitin kwararru na Yariman Bakura, ma’aikatan lafiya da dama a wasu asibitocin jihar ma suna bin bashin albashi na tsawon watanni.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN