An kori wani dan uwa da ’yar uwa daga unguwarsu da ke garin Lude, Mbaise a jihar Imo, bisa zarginsu da aikata lalata.
Wani faifan bidiyo da aka raba ta yanar gizo ya nuna mambobin al'umma suna jagorantar fitar da 'yan'uwan daga cikin al'umma tare da ƙananan kayaki da suke da su.
Yan banga da ake kira Akagu suna wajen domin fitar da su daga cikin al’umma.
Daga nan aka gargade su da kar su dawo.
An ji wata murya tana bayyana a cikin bidiyon dalilin da yasa aka kore su: "Saurayin yana aikata lalata da yar uwarsa."
An umarce su su je duk inda suke so amma kada su koma garin Lude a kowane hali.