An karya lagon tsageru: An yi bata kashi da 'yan bindiga, an hallaka tsageru 4 nan take


Rundunar Operation Forest Sanity ta hallaka wasu ‘yan ta’adda hudu tare da kwato makamai da wasu kayayyakin aikata kaifi a jihar Kaduna. Legit.ng ta wallafa.

Wannan na fitowa ne daga bakin Manjo Janar Musa Danmadami, daraktan yada labarai na gidan soja a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata a Abuja.

Danmadami ya bayyana cewa, jami’an tsaron sun kuma dakile harin ‘yan bindiga a yankin Rafin Sarki a karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna a ranakun Lahadi da Litinin.

Ya kuma kara da cewa, an fatattakin ‘yan bindiga tare da kashe biyu da kuma kwato makami AK-47.

Ya kada da cewa, rundunar a ranar Talata ta yi kwanton bauna ga ‘yan bindiga kan wasu ‘yan bindiga a kauyen Rafin Taba, inda aka kashe ‘yan ta’adda biyu.

Ya ce jami’ai sun kwato bindigogi AK-47, alburusai, wayoyin hannu, adda, babura guda biyu da kudi N206,000.

Sanarwar ta ce:

"Babban ofishin rundunar sojoji ta yabawa dakarun Operation Forest Sanity kuma tana karfafawa jama'a gwiwa da su ba sojoji sahihan bayanan ‘yan ta’adda masu aikata laifuka.”

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN