Yan sandan sun kama matar da ta buge yaro da itace a kai ya mutu a jihar Kebbi


Rundunar Yan sandan jihar Kebbi karkashin Kwamishinan Yan sandan jiharCP Ahmed Magaji Kontagora, ta kama wata mata bayan ta yi amfani da katako ta kwade yaro mai shekara 3 da haihuwa har Lahira. Shafin isyaku.com ya wallafa.

Kwamishinan ya yi bayanin hakan ga manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Gwadangaji, da kuma sanarwar manema labarai da ya fito daga ofishinsa ranar Talata. 

Sanarwar ta ce:

"A ranar 2 ga Disamba, 2022 da misalin karfe 7pm, wata Zara'u Sahabi 'f' 'yar shekara 25 a kauyen Kwaku, gundumar Kaoje, a karamar hukumar Bagudo, a dakinta, ta yi amfani da itace ta buga wani Gadafi Nasiru 'm' mai shekaru 3 a duniya.a  kai.  Sakamakon haka, ya mutu nan take.  

Bayan samun rahoton, tawagar ‘yan sanda ta garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka cafke wanda ake zargin.  

A yayin gudanar da bincike, ta amsa laifin ta.  Za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu bayan an kammala bincike."

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN