Yan bindiga sun kashe basarake a Zamfara bayan sun yi masa kwanton baunai

Yan bindiga sun yi wa Sarki a Zamfara kwanton bauna suka kashe shi


Wasu ‘yan bindiga sun kashe Hakimin Yankuzo, Alhaji Hamza Abdullahi Kogo na Masarautar Tsafe a jihar Zamfara.

Majiyoyi sun shaida wa gidan Talabijin na Channels cewa ‘yan bindigar sun kai wa hakimin hari a kan hanyarsa ta komawa al’ummarsa daga wata ganawar hukuma da aka yi ranar Juma’ar da ta gabata 9 ga watan Disamba da misalin karfe 8 na dare.

An harbe shi tare da raunata shi a yunkurin sace shi.  An garzaya da Kogo zuwa cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Gusau, babban birnin jihar inda daga bisani ya rasu a daren Asabar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN