Kwamishinan Yan sandan jihar Kebbi ya kaddamar da kwamiti mai matukar mihimmanci gabanin zaben 2023


Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kebbi, CP Ahmed Magaji Kontagora, ranar Laraba 9/12/2022, ya gayyaci shuwagabannin hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki kan zaben 2023 a Aberta guest inn Birnin kebbi, domin gudanar da wani taro, inda ya yaba da yadda za a tabbatar da gaskiya, sannan an tattauna lamurra kan kalubalen ga zabuka da kuma mafita masu karbuwa a zaben 2023. Shafin isyaku.com ya ruwaito.

Biyo bayan fara gangamin yakin neman zabe daga dukkan jam'iyyun siyasa, fagen siyasa na aiki a halin yanzu kuma yuwuwar karuwar rashin zaman lafiyar siyasa na iya karuwa a fadin jihar. 

CP Ahmed Magaji Kontagora ya kaddamar da kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin tsaro a yayin taron, bisa ga umarnin babban sufeton ‘yan sanda, IGP Usman Alkali Baba. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN