Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kebbi, CP Ahmed Magaji Kontagora, ranar Laraba 9/12/2022, ya gayyaci shuwagabannin hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki kan zaben 2023 a Aberta guest inn Birnin kebbi, domin gudanar da wani taro, inda ya yaba da yadda za a tabbatar da gaskiya, sannan an tattauna lamurra kan kalubalen ga zabuka da kuma mafita masu karbuwa a zaben 2023. Shafin isyaku.com ya ruwaito.
Biyo bayan fara gangamin yakin neman zabe daga dukkan jam'iyyun siyasa, fagen siyasa na aiki a halin yanzu kuma yuwuwar karuwar rashin zaman lafiyar siyasa na iya karuwa a fadin jihar.
CP Ahmed Magaji Kontagora ya kaddamar da kwamitin tuntuba tsakanin hukumomin tsaro kan harkokin tsaro a yayin taron, bisa ga umarnin babban sufeton ‘yan sanda, IGP Usman Alkali Baba.