Kotu ta kori Wali, ta tabbatar da Abacha matsayin dan takarar Gwamnan PDP a Kano


Babban kotun tarayya da ke zamanta a Kano, a ranar Alhamis, ta tabbatar da Mohammed Sani Abacha, a matsayin halastacen zababben dan takarar gwamna na PDP a jihar Kano. Legit.ng ta ruwaito.

A hukuncinsa, a yammacin ranar Alhami, Mai sharia A.M. Liman ya soke zaben cikin gida da jam'iyyar ta yi inda Sadik Aminu Wali ya yi nasara.

Kotun ta kuma umurci hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta cire sunan Wali ta maye da na Mohammed Sani Abacha, rahoton The Punch.

Kotun ta amsa dukkan bukatun da mai shigar da kara ya nema a masa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN