Da dumi-dumi: Yan sandan jihar Kebbi sun kama wasu mutane biyu da laifin yi wa kananan yara yan mata fyade


Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta kama wasu mutane biyu da laifin yi wa wasu kananan yara biyu fyade a kananan hukumomin Danko/Wasagu da Augie (LGAs) na jihar. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

Daya daga cikin wadanda ake zargin Mista Christopher Pills mai shekaru 30 a garin Bena da ke karamar hukumar Danko/Wasagu ta jihar an kama shi ne bayan mahaifin yarsa mai shekaru 9 da haihuwa, Mista Lawrence Johnson, ya ruwaito cewa Pills ya lalata ‘yarsa.

Shi kuma wanda ake zargin Anas Dantalli mai shekaru 19 a Nawada Illela Kwaido a karamar hukumar Augie, an kama shi ne bayan wani mai suna Mista Rugga Aliyu na Mashekari Illela Kwaido, karamar hukumar Augie, ya kai rahoto a hedikwatar ‘yan sanda da ke Augie cewa wanda ake zargin ya bi ‘ya’yansa ne a lokacin da suke kiwon awaki da tumaki a cikin daji, ya yi wa daya daga cikinsu fyade.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Ahmed Magaji-Kontagora ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kuma za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN