Type Here to Get Search Results !

"Ba zan kara karanta labaran soshiyal midiya ba don yana tayar min da hankali da fushi" - Tinubu


Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Ahmed Tinubu, ya bayar da dalilan da ya sa ya daina maida hankali kan kasidu da labarai da kuma batutuwan da suka taso a shafukan sada zumunta. Jaridar Vanguard ta ruwaito.

Tsohon gwamnan na Legas ya bayyana cewa karanta labarai a shafukan sada zumunta na ba shi ‘hawan jini’.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya bayyana hakan a wani faifan bidiyo da daya daga cikin abokansa, Ademola Oshodi ya wallafa a shafinsa na Twitter.

A cikin faifan bidiyon, tsohon gwamnan jihar Legas ya ce yakan yi fushi a duk lokacin da ya karanta labarai a shafukan sada zumunta. 

“Ba na kara karanta labaran kafafen sada zumunta;  suna yi min zagin fitar hankali. Idan na karanta, yakan haddasa min tashin hankali kuma da fushi".

 “Ba na karanta shi, don haka idan ina son jin wani abu;  'Ya'yana ko ma'aikata na za su faÉ—i wannan nayan sun karanto, in na gaji, na ce don Allah a manta da shi."

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies