An tsinci gawar wani matashi da ya bace, an datse masa mazakuta an kwakwale idanunsa a wata jihar arewa



An gano gawar wani matashi da ya bace kusan kwanaki hudu.  Jikinsa babu wasu sassa.

Lamarin ya faru ne a yankin Babale da ke karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato.

An gano gawar ne a ranar Juma’a kuma aka binne gawar a ranar Asabar.

Wani mazaunin garin da ya so a sakaya sunansa ya ce: “Lamarin ya faru ne a Kururuwan ka banza, dajin mai kauri tsakanin Zakaliyo da Babale.

“Yaron mai shekaru tsakanin 19 zuwa 21, ya yi batan dabo tsawon kwanaki hudu.

“A rana ta bakwai da ake bincike, an tsinci gawar yaron a daya daga cikin duhuwar Kururuwan ka banza tare da cire masa idanu biyu, da kuma azzakarinsa.

"An binne gawar a wurin da suka tsinci gawar, saboda gawar ta ruba."

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Alfred Alabo, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “Rundunar ta na sane da abin da ya faru a Babale.  DPO na yankin da tawagarsa suna aiki a kai don bankado wadanda ke da hannu a wannan aika aika.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya fusata da irin wannan lamari kuma ba za a bar wani dutse ba wajen gurfanar da wanda ya aikata laifin.”

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN