Mutum 1m: Magoya bayan tsohon shugaban Majalisar Dattawa sun rufe Argungu

Mutum 1m: Magoya bayan tsohon shugaban Majalisar Dattawa sun rufe Argungu


Magoya bayan tsohon shugaban Majalisar Dattawa Dr Yahaya Abdullahi a ranar Lahadi sun rufe garin Argungu da ke karamar hukumar Argungu a jihar Kebbi a tattakin mutum miliyan daya.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa taron da ya samu halartar mahalarta daga sassan jihar Kebbi ta Arewa, ya kawo tsaikon kasuwanci da sauran harkokin kasuwanci a yankin.

NAN ta kuma ruwaito cewa Sen. Adamu Aliero (PDP Kebbi Central) kuma dan takarar Gwamna na PDP a Kebbi, Maj.-Gen. Aminu Bande, na daga cikin manyan baki da suka halarci bikin.

Da yake jawabi ga taron, Aliero ya shawarci magoya bayansa da su kasance da jajircewa, mayar da hankali, addu’a tare da bin doka.

Shima da yake nasa jawabin, tsohon shugaban jam’iyyar APC na jihar Kebbi, Alhaji Bala Sani-Kangiwa, ya ce an shirya tattakin ne domin nuna goyon baya ga tsohon shugaban Majalisar Dattawa domin samar da wakilci mai inganci.

A nasa bangaren, Bande ya bayyana tsare-tsarensa na ci gaban jihar, idan aka zabe shi.

Sun hada da karfafa tattalin arziki, samar da guraben ayyukan yi, ba da damammakin noma da bunkasa ilimi.

Da yake mayar da martani, Abdullahi ya yabawa wadanda suka shirya taron tare da ba su tabbacin ci gaba da samun wakilci mai ma’ana a Majalisar Dattawa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN