Gwamnatin Zamfara ta rufe NTA Gusau, Prime FM, da sauran su, duba dalili

Gwamnatin Zamfara ta rufe NTA Gusau, Prime FM, da sauran su, duba dalili


Gwamnatin Zamfara ta bayar da umarnin rufe gidan talabijin na Nigerian Television Authority (NTA) Gusau da Pride FM na Gidan Rediyon Najeriya (FRCN) bisa zargin karya dokar gwamnati da aikin jarida.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai Alhaji Ibrahim Dosara ya fitar a Gusau ranar Asabar.

Kwamishinan ya ce sauran kungiyoyin yada labaran da aka sanya wa takunkumi sun hada da Gamji TV da Gamji FM da kuma Al umma TV wadanda ke zaman kansu.

Dosara ya ce kwamitin tsaro na jihar ya amince da rufe tashoshin.

A cewarsa, an umurci kwamishinan ‘yan sandan da ya kama tare da gurfanar da jami’an ofishin da lamarin ya shafa da aka kama suna karya dokar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN