An kama wasu mata 'yan Najeriya 8 a kasar Libya bisa zarginsu da karuwanci




An kama wasu mata 8 'yan Najeriya a kasar Libya bisa zarginsu da yin karuwanci. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

A cewar Migrant Rescue Watch, ‘yan sanda sun kai samame a wani gida a gundumar Kufra inda suka kama matan da laifin karuwanci.

An kuma kama wani dan Najeriya da aka ce dan fashi ne yayin samamen.

‘’Yan sanda biyo bayan bincike da sammacin mai gabatar da kara sun kai samame wani gida a Kufra tare da kama wasu bakin haure 9 da suka hada da mata 8 ‘yan asalin Najeriya bisa zargin karuwanci.

Dukkansu an mika su ga hukumar tsaro domin hukunta su. kungiyar ta sanar da haka a ranar Alhamis, 6 ga Oktoba, 2022. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN