Type Here to Get Search Results !

An kama wasu mata 'yan Najeriya 8 a kasar Libya bisa zarginsu da karuwanci




An kama wasu mata 8 'yan Najeriya a kasar Libya bisa zarginsu da yin karuwanci. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.

A cewar Migrant Rescue Watch, ‘yan sanda sun kai samame a wani gida a gundumar Kufra inda suka kama matan da laifin karuwanci.

An kuma kama wani dan Najeriya da aka ce dan fashi ne yayin samamen.

‘’Yan sanda biyo bayan bincike da sammacin mai gabatar da kara sun kai samame wani gida a Kufra tare da kama wasu bakin haure 9 da suka hada da mata 8 ‘yan asalin Najeriya bisa zargin karuwanci.

Dukkansu an mika su ga hukumar tsaro domin hukunta su. kungiyar ta sanar da haka a ranar Alhamis, 6 ga Oktoba, 2022. 

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Below Post Ad

Hollywood Movies