Fitaccen jarumin fina-finan Hausa na Kannywood, Umar Yahaya Malumfashi 'ka fi gwamna' ya rasu




Da yammacin nan ne aka samu labarin rasuwar fitaccen jarumin fina-finan Hausa, Malam Umar Yahaya Malumfashi. Jaridar leadership ta ruwaito.

Marigayin ya kasance fitaccen jarumi da ya taka rawa a fina-finan Hausa da dama ciki har da shirin nan mai dogon zango da ake haskawa a gidan Talabijin na Arewa24, Kwana Casa’in.

Ya rasu ne a yau Talata bayan ya yi fama da jinya.

Ko a makon jiya sai da aka yi masa hasashen mutuwa wanda daga bisani ya fito ya karyata, kana ya nemi a taya shi da addu’a.

Daya daga cikin masu harkar fim, Nasiru Sa’ad Gwangwazo wanda har ila yau shi ne Editan Jaridar Blueprint Manhaja, ya wallafa ta’aziyyar rasuwar marigayin a shafinsa na facebook wanda yake kara tabbatar da labarin rasuwarsa.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN