Marigayin ya kasance fitaccen jarumi da ya taka rawa a fina-finan Hausa da dama ciki har da shirin nan mai dogon zango da ake haskawa a gidan Talabijin na Arewa24, Kwana Casa’in.
Ya rasu ne a yau Talata bayan ya yi fama da jinya.
Ko a makon jiya sai da aka yi masa hasashen mutuwa wanda daga bisani ya fito ya karyata, kana ya nemi a taya shi da addu’a.
Daya daga cikin masu harkar fim, Nasiru Sa’ad Gwangwazo wanda har ila yau shi ne Editan Jaridar Blueprint Manhaja, ya wallafa ta’aziyyar rasuwar marigayin a shafinsa na facebook wanda yake kara tabbatar da labarin rasuwarsa.
Rubuta ra ayin ka