An kama wani matashi dan shekara 27 da laifin lalata da yarinya ‘yar shekara 3 a Arewa, duba abin da ya faru


Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wani matashi dan shekara 27 mai suna Mato Yohannah da laifin lalata da wata yarinya ‘yar shekara 3 a karamar hukumar Ganjuwa da ke jihar. 

Shafin labarai na isyaku.com ya samo cewa Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Ahmed Mohammed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, 30 ga watan Agusta, 2022.

"A ranar 24 ga watan Agustan 2022 da misalin karfe 11 na safe, wani Mato Yohannah 'm' mai shekaru 27 a kauyen Jimbin, karamar hukumar Ganjuwa jami'an tsaro na hedikwatar Ganjuwa sun kama shi bayan ya yi lalata da wata (sara Ezra), ba ainihin sunanta bane 'f' mai shekaru 3yrs . na kauyen Jimbin, karamar hukumar Ganjuwa," in ji PPRO. 

“A binciken da ake yi, wanda ake zargin ya amsa laifin yi wa kananan yara fyade a karo na biyu, haka kuma za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin gurfanar da shi gaban kuliya".

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN