Shahararren Mawaki Davido,yi godiya ta musamman ga shugaba Muhammadu Buhati bayan Kawunsa ya lashe zaben Gwamnan jihar Osun da aka kammala ranar Asabar. Ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter inda ya yi addu’a ga shugaba Buhari da ya ba shi damar gudanar da sahihin zabe da ya sa kawunsa, Ademola Adeleke ya fito a matsayin Gwamnan jihar Osun. Shafin labarai na isyaku.com ya samo.
Davido ya yi addu’ar ne a lokacin da yake mayar da martani ga kalaman shugaba Buhari inda ya taya Adeleke murna kuma ya bayyana cewa ya kuduri aniyar barin gadon zabe na gaskiya da adalci.
Duba kalamansa a kasa...