Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ba za a kakaba dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC a zaben 2023 mai zuwa ba, TheCable ta ruwaito
A cewar wata sanarwa da Garba Shehu, mai magana da yawun shugaban kasa Buhari ya fitar, Buhari ya bayyana haka ne a ranar Litinin a wani taro da gwamnonin APC na yankin Arewa suka yi.
Kalaman shugaban na zuwa ne a daidai lokacin da rahotanni ke cewa Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya amince da shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan a matsayin dan takarar jam’iyyar.
A cewar sanarwar:
“An zabe ka kamar yadda aka zabe ni. Ka zama mai hankali kamar yadda nake. Allah ya bamu dama; ba mu da dalilin korafi. Dole ne mu kasance a shirye don daukar zafi kamar yadda muke daukar farin ciki. A bar wakilai su yanke shawara. Dole ne jam’iyyar ta shiga, babu wanda zai nada kowa.”