Tsohon gwamna jihar Legas, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya lashe zaben fidda gwanin yan takaran shugaban kasa karkashin jam'iyyar All Progressives Congress APC.
A zabensa na faako tun bayan barin muli a 2007, Tinubu yanzu shine zai wakilci jam'iyyar PDP a zaben shugaban kasa a zaben shekarar 2023.
Tinubu ya lallasa yan takara 12 da suka fafata a zaben inda ya samu kuri'u sama da 1000
Wanda ya zo na biyu shine tsohon Gwamnan jihar Rivers, kuma tsohon Ministan Sufuri Rotimi Amaechi wanda ya samu kuri'u 316.
Sannan Farfesa Yemi Osinbajo wanda ya samu kuri'u 235.
Tinubu yanzu zai fafata da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, na jam'iyyar Peoples Democratic Party PDP da Rabiu Musa Kwankwaso na jam'iyyar NNPP dss a ranar 25 ga Febrairu, 2023.
Ga jadawalin sakamakon:
S/N Sunayen yan takara Adadin Kuri'in da suka samu
1 Asiwaju Bola Tinubu 1213
2 Rotimi Amaechi 316
3 Farfesa Yemi Osinbajo 235
4 Ahmad Lawan 152
5 Yahaya Bello 47
6 Sani Ahmed Yarima 4
7 Ben Ayade 37
8 Rochas Okorocha 0
9 Tunde Bakare 0
10 Tein Jack Rich 0
11 Ogbonnaya Onu 1
12 Dave Umahi 38
13 Emeka Nwajuiba 1