Kamar yadda NAN ta ruwaito, bangarorin biyu sun bayyana a gaban wata kotun shari’ar musulunci a jihar Kaduna a ranar Litinin 6 ga watan Yuni.
Wanda ya shigar da karar ya shaidawa kotu cewa yana da alaka da jarumar kuma ta yi alkawarin aurensa.
“Ya zuwa yanzu na kashe mata Naira 396,000, duk lokacin da ta nemi kudi ina ba ta ba tare da bata lokaci ba da fatan za mu yi aure, ita ma ta kasa fitowa a Gusau da ke Zamfara inda nake zaune bayan na yi duk wani shiri da na yi na karbe ta,” inji Musa.
An fara sauraren karar ne a ranar 23 ga watan Mayu amma wanda ake kara bata kasance a gaban kotu.
A nata bangaren, wanda ake kara wanda ya samu wakilcin Lauyanta, Mista Mubarak Kabir ya bayyana cewa wanda yake karewa ba ta da tabbacin sahihancin sammacin.
"Matsayin wacce nime katewa na shahararru yana jawo mutane daban-daban masu niyya daban-daban. Ta kasance mai taka-tsan-tsan game da tsaron lafiyarta," in ji Kabir.
Kabir ya roki kotu da ta kara masa lokaci domin gabatar da wanda yake karewa a kotu.
Alkalin kotun, Malam Rilwanu Kyaudai, ya dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yuni 2022.