Dan takarar jam'iyar APC ya lashe zaben Gwamnan Ekiti ya ci kananan hukumomi 15 cikin 16


Biodun Oyebanji, tsohon sakataren gwamnatin jihar Ekiti, ya tabbata wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Ekiti.

Kayode Oyebode, baturen zaben da aka yi a ranar Asabar, ya sanar da sakamakon zaben a sa'o'in farko na ranar Lahadi, Daily Trust ta ruwaito.

Oyebanji ya samu kuri'u 187,057 inda ya lallasa manyan masu kalubalantarsa, Segun Oni na jam'iyyar SDP wanda ya samu kuri'u 82,211 da Bisi Kolawole na jam'iyyar PDP wanda ya samu kuri'u 67,457.

Fafesa Kayode Oyebode, baturen zaben, ya bayyana Oyebanji a matsayin wanda yayi nasarar lashe zaben a wurin karfe 3:04 na safiyar Lahadi.

Jimillar 'yan takara 16 ne aka samu suka yi takarar kujerar gwamnan. An samu kuri'u masu amfani 351,865, kuri'u da suka lalace 8,888 sai jimillar kuri'un da aka kada sun kai 360,753.

Ga sakamakon karashe na zaben:

A: 166


AAC: 409


ADC: 5,597


ADP: 3,495


APC: 187,057


APGA: 376


APM: 290


APP: 1,980


LP: 195


NNPP: 529


NRM:347


PDP: 67,457


PRP: 856


SDP: 82,211


YPP: 618


ZLP: 282


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN