Da dumi-dumi: Sojoji sun gano wata mata da Boko Haram suka sace tun 2014


Dakarun runduna ta 26 Task Force Brigade, a ranar Talata, sun gano wata wata Mary Ngoshe, wacce a cewar rundunar sojin Najeriya, tana daya daga cikin ‘yan matan da aka yi garkuwa da su a makarantar Sakandaren ’yan mata ta gwamnati da ke Chibok a shekarar 2014.

Ngoshe, wadda aka same ta da wani yaro da ake kyautata zaton nata ne, sojojin sun tare ta ne a lokacin da suke sintiri a kewayen Ngoshe a jihar Borno.

Hakan na kunshe ne a wani sako da rundunar ya wallafa a shafin Twitter a safiyar Laraba.

Sakon ya ce:

“Dakarun 26 Task Force Brigade da ke sintiri a kewayen Ngoshe a jihar Borno a ranar 14 ga watan Yuni 2022 sun gano wata mata Mary Ngoshe da danta. Ana kyautata zaton tana daya daga cikin ‘yan matan da aka sace daga GGSS Chibok a 2014. Ana ci gaba da bincikarta.”

Karin bayani na nan tafe...

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN