Jam’iyyar PDP ta amince da sake zaben fidda gwani a mazabar tarayya da na Jihohi na jihohin Legas, Imo, Benue da Katsina domin tantance ‘yan takara a zaben 2023 mai zuwa. NAN ta ruwaito.
Jam’iyyar ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a daren Juma’a ta hannun sakataren yada labaranta na kasa, Debo Ologunagba, a Abuja.
Shafin labarai ta yanar gizo na isyaku.com ya tattaro cewa Ologunagba ya ce bayan tattaunawa mai zurfi kan rahotannin kwamitin zabe da daukaka kara kan majalissar PDP a jihohin Legas, Imo, Benue da Katsina, kwamitin ayyuka na kasa (NWC) ya amince da sake zaben fidda gwani.
Ya ce hukumar ta NWC ta amince da ranar Lahadi 5 ga watan Yuni domin sake zaben fidda gwani a mazabar Ahiazu da Orsu na jihar Imo; da kuma Musawa, Dandume, Zango dake jihar Katsina.
Sauran a cewarsa sun hada da: Mazabun tarayya na Oru East/Orsu/Orlu, da Kwande/Ushongo na jihar Benue.
Haka kuma a ranar litinin 6 ga watan Yuni domin gudanar da zaben fidda gwani na majalisar wakilai ta jihar Legas (Mazabu 24 na tarayya).
“Bugu da kari kuma, Sanatan Kaduna ta tsakiya a jihar Kaduna, Sanatan Enugu ta Yamma na jihar Enugu da kuma mazabar tarayya ta Boki/Ikom da kuma mazabar Jahar Yakuur II, dukkansu na Cross River da aka shirya yi a ranar Asabar 4 ga watan Yuni an soke su,” inji shi.
Ya shawarci daukacin ‘ya’yan jam’iyyar na jihohin da abin ya shafa da su lura da sabbin ranakun.