Rahotanni daga babban Kotun jihar Kebbi na cewa an gurfanar da Idris Suleiman a gaban Kotu, bisa tuhumar kisan Sadiya Idris tare da diyarta a Unguwar Labana a garin Birnin kebbi.
An tarar da gawar Sadiya tare da diyarta ranar 11 ga watan Aprilu bayan an sareta a wurare da dama kuma aka kashe diyarta duk a gidan mijinta da ke Unguwar Labana shiyar tagwayen titin Sani Abaca da ke Birnin kebbi.
Idris tare da rakiyar jami'an kula da gidajen gyara hali sun kawo shi gaban Kotu sanye da farar Kaftani shedda kuma babu hula a kansa.
Bayan sauraron shaidu, Kotu ta dage shari'ar har ranar Laraba 15 ga watan Yuni 2022 domin ci gaba da shari'ar.