Hotuna: Shugaba Buhari ya yi ganawar bankwana da Ministoci da suka sauka daga mukamansu domin neman mukaman siyasa


A safiyar yau ne shugaba Buhari ya gudanar da wani zama na ban kwana ga ministocin da suka bar majalisar ministocinsa domin neman mukaman zabe a zaben 2023 mai zuwa.


A wajen taron valedictory wanda aka gudanar a zauren majalisar da ke Abuja, Shugaba Buhari ya gode wa ministocin bisa hadin kan da suka ba shi, yayin da ya hori sauran mambobin majalisar da su kara himma da jajircewa wajen samun nasarar gwamnatin.


Wadanda suka halarci taron sun hada da karamin ministan ma’adinai da karafa Uche Ogar; Karamin Ministan Albarkatun Man Fetur, Timipre Sylva; Ministan kwadago da samar da ayyukan yi, Chris Ngige; Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; Ministar harkokin mata Pauline Tallen.

Sauran sun hada da ministan harkokin Neja Delta, Goodwill Akpabio; Ministan shari'a kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami da ministan kimiyya, fasaha da kirkire-kirkire, Ogbonnaya Onu.


Mutane tara sun kasance a jiki yayin da tsohon karamin ministan ilimi, Emeka Nwajiuba, wanda shi ne na goma wanda bai sami halartar taron ba amma da dalili . 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN