Da duminsa: 'Yan uwan fasinjojin jirgin kasan Abuja-Kaduna sun fito zanga-zanga


Iyalan fasinjojin da aka sace yayin da suke kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna sun balle zanga-zanga a babban birnin tarayya ta Abuja.

Wannan ne karo na farko da 'yan uwan wadanda aka sacen suka fito zanga-zanga tun bayan faruwar ibtila'in, Punch ta ruwaito.

A ranar 28 ga watan Maris din 2022, 'yan ta'adda sun kai mugun hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna kuma hakan ya yi sanadin mutuwar a kalla mutum takwas yayin da 26 suka jigata kuma aka yi garkuwa da wasu.

Iyalan sun ce zanga-zangar sun fito ta ne sakamakon barazanar da 'yan ta'adda suka yi na cewa za su fara halaka wadanda ke hannunsu idan har ba a cika sharuddansu.

Sun yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari, hafsoshin tsaro da kungiyoyin duniya da su kawo musu dauki.

Karin bayani na nan tafe...

AK9Train: Miyagu sun tuntubi kakakin Sheikh Gumi, sun ba FG wa'adin kwana 7 ko su aiwatar da nufinsu

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN