Mai Alfarma Sarkin Musulmi,Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya yi Allah-wadai bisa abinda ya auku a kwalejin ilmin Shehu Shagari dake Sokoto wanda yayi sanadiyar rashin rayuwar daliba.
Masarautar Sarkin Musulmi a jawabin da ta saki tace:
Masarauta ta samu labarin abin takaicin abubuwan dake faruwa a kwalejin ilmin Shehu Shagari dake Sokoto da ya kai ga mutuwar dalibar makarantar."
Masarauta ta yi Allah-wadai da lamarin gaba daya kuma ta yi kira ga jami'an tsaro su hukunta wadanda suka aikata wannan abu."
Masarautar na kira ga daukaci jama'ar jihar su zauna lafiya da juna."
Latsa nan ka saurara 👇
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=10221449412999857&id=1086336452