Ministan shari'a kuma Antoni Janar na Najeriya Abubakar Malami SAN bai sauka daga mukaminsa ba. Shafin labarai na isyaku.com ya sami tabbacin haka daga majiya mai tushe.
Majiyar ta ce "Ministan shari'a bai sauka daga mukaminsa ba, yanzunnan ya bar office. Wannan zancen ba gaskiya bane"
Labarai na ta zagayawa a shafukan sada zumunta na Facebook cewa Ministan shari'a ya sauka daga mukaminsa. Sai dai ta tabbata cewa zancen ba gaskiya bane.