Tonon asiri: Sojojin Najeriya sun kama jami’an tsaro da ke kai wa ‘yan bindiga kudin fansa a Kaduna


Rundunar sojin Najeriya ta kama jami’an tsaro da ke kai wa ‘yan bindiga kudin fansa a Kaduna.

Dakarun hadin guiwa sun kama Naira miliyan 60 da ake kai wa masu laifi a matsayin kudin fansa domin ’yancin wadanda aka kama.

Wasu daga cikin wadanda aka kama suna kai wa Yan bindigan kudin fansar jami'an tsaro ne.

Sojoji sun gudanar da ayyukan sirri, sun kuma ceto wadanda aka yi garkuwa da su da suka hada da mata da kananan yara.

Hare-haren da rundunar sojojin Najeriya da na rundunar sojojin sama na musamman ta NAF suka kai, ta yi nasarar fatattakar 'yan bindigar da dama.

Tawagar ta hada da 271 NAF a Birnin Gwari da Army Forward Operating Base (FOB) a Gwaska, Kaduna.

“An kwato tsabar kudi N60,000,000, da kayayyakin man fetur da kuma nagartattun makamai, a yayin gudanar da aikin,” wani jami’in ya shaida wa PRNigeria.

“Za mu mika shari’ar ‘yan aike da aka kama, wadanda suke da shaidar jami’an tsaro, zuwa ga hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da kuma hukumar leken asiri ta tsaro (DIA) domin ci gaba da bincike”.

Sojojin sun kuma kwato motoci da bindigogi kirar AK-47 da mujallu da alburusai iri-iri da wayoyin hannu.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN