Malaman addini 6 sun rasu a hadarin mota a hanyarsu ta dawowa daga da'awa a Kano


Malaman addinin Musulunci masu wa'azi guda shida sun rasa rayukansu a jihar Kano ranar Laraba sakamakon mumunan hadarin mota yayin dawowa daga wajen da'awa.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa Malaman sun yi hadarin mota ne na hanyar komawarsu gida daga karamar hukumar Sumaila. Rahotun legit.

Wata jami'in gidauniyar Imam Malik da suka dauki nauyin da'awar ta bayyana cewa sun samu labarin hadarin ne misalin karfe 3 na rana.

A cewarta, labarin da suka samu shine dukkan Malamai shida dake cikin tawagar da'awar sun rigamu gidan gaskiya.

Ta ce har yanzu ba'a samu bayanai kan sauran wadanda suka raka malaman ba.

Tace:

"Mun taru yanzu a gidauniyar dake unguwar Dakata. Zamu je gidan Sheikh Alkassim Zakariyya don jana'izarsu."

Wasu daga cikin dalibansu sun yi jimamin rashin malaman a shafin ra'ayi da sada zumuntar Facebook.

An tattaro cewa daga cikin wadanda suka rasu akwai Sheikh Alkassim, Isiya Tela, Malam Ishaq Rummawa, da Mustapha Musa Sa’ad.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN