Wasu jami’an ‘yan sandan da suka cire sunayensu daga tag na suna a tufafin aiki, sun fuskanci ladabtarwa daga babbansu.
Mukaddashin Kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya Prince Olumuyiwa Adejobi, ya ce an kama jami’an ‘yan sandan ne a lokacin da ake gudanar da bincike na yau da kullum. Ya bayyana cewa da gangan ne suka cire sunayensu domin kauce wa tantancewa.
Kakakin ‘yan sandan ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa;