Siyasar Kebbi: Kotu ta ce bata da hurumin sauraron karar rikicin jam'iyar APC na jihar Kebbi, duba abin da ya faru (Bidiyo)


Kotu a jihar Kebbi ta ce bata da hurumin sauraron karar da wasu mambobin jam'iyar APC reshen jihar Kebbi suka shigar a gabanta watannin da suka gabata.

Alhaji Bala Sani Kangiwa ya sanar da haka a wani faifen bidiyo da ke yawatawa a shafukan sada zumunta wanda Yusha'u Nata'ala ya nada jim kadan bayan fitowa daga Kotun a garin Gwadangaji.

Jam'iyar APC reshen jihar Kebbi ta tsunduma cikin rikici da ya kai ga sauke wasu shugabanninta yan watanni da suka gabata. Sakamakon haka wadanda suke ganin ba a yi masu daidai ba suka garzaya Kotu.

Latsa kasa ka kalli cikakken bayanin abin da ya faru a Kotu.
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN