Yanzu yanzu: An kama maigida da matarsa da sassan Dan Adam a cikin dakinsu, duba abin da ya faru




Jami'an rundunar yansandan jihar Ogun, ranar Asabar 12 ga watan Fabrairu, sun kama wani mutum mai suna Kehinde Oladimeji dan shekara 43 da matarshi mai suna Adejimoke Raji mai shekara 35, bisa zargin mallakar  danyen sassan jikin dan adam.

Jami'an yansandan shiyar Kemta ne suka kama ma'auratan a gidansu da ke lamba.72 MKO Abiola way, Leme Abeokuta, bayan Baale na al'umman Leme mai suna Moshood Ogunwolu ya kai kara wajen yansanda bayan an dinga jiyo mugun wari yana busowa daga dakin ma'auratan.

Sakamakon haka DPO na yansandan Kemta Division, CSP Adeniyi Adekunle, ya jagorancin jami'ansa zuwa gidan ma'auratan inda suka gudanar da bincike kuma aka gano sassan bil'adama a dakin maauratan.

Yansanda na ci gaba da gudanar da bincike kasancewa ma'auratan sun ce wani mutum ne ya kawo masu sassan jikin Dan Adam domin gudanar da tsafi saboda su matsafa ne.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN