Ma'aikacin gidan yari ya yi wa yarinya yar shekara 13 mai tabin hankali fyade, duba abin da ya faru



An kama wani jami'in kula da gidan yari mai suna M. C. Bello, bisa zargin yi wa wata yarinya yar shekara 13 mai tabin hankali fyade a jihar Adamawa.

Rahotanni na cewa Bello ya rudi yarinyar da N50 ta biyoshi zuwa dakinsa da ke gidajen ma'aikatan gidan yari na Yolde-Pate da ke karamar hukumar Yola ta kudu inda ya yi mata fyade.

Kakakin hukumar yansandan jihar Adamawa DSP Suleiman Nguroje ya tabbatar wa manema labari faruwar lamarin.

Ya ce yansanda sun kama Bello kuma suna gudanar da bincike kan lamarin.

Wata hafsa mai suna Madam Laila, wacce ke sashen kare hakkin Dan Adam na Centre for Women and Adolescent Empowerment, ta ce an gudanar da bincike kan yarinyar kuma sakamakon binciken Asibiti ya tabbatar cewa an keta budurcinta.

Ta sha alwashin cewa za su bi diddigin shariar har zuwa karshensa domin ganin an yi wa yarinyar adalci.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN