An kashe jami’in ne a lokacin da ‘yan bindiga suka kaddamar da hari a caji ofis din da yammacin ranar Juma’a.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Michael Abattam, ya tabbatar da faruwar harin amma ya ce an dakile harin.
“A ranar 14 ga watan Janairu, 2022 da misalin karfe 20:45, rundunar ‘yan sanda ta ofishin ‘yan sanda na Mgbidi, ta dakile wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a wata farar mota kirar hilux, inda suka yi yunkurin kutsawa cikin ofishin, amma jami’an sun dakile harin, yayin da ‘yan bindigan suka tsira da raunukan harbi daban-daban.
Leadership Hausa
Reported by ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g
Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN
Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN
Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN
Shafukan sada zumunta
Twitter twitter.com/isyakalabari
Facebook facebook.com/isyakalabari