Wasu ‘yan bindiga a kan babura, kowannen su dauke da mutum2, sun kai hari a yankin Gbagyi Villa a daren ranar Litinin din da ta gabata.
Yankin dai yana kan hanyar zuwa matatar mai ta Kaduna ne, inda suka kashe mutum daya tare da yin garkuwa da matarsa da wasu.
Ya zuwa yanzu, 'yan jarida suna jiran martanin hukuma daga hukumomin tsaron kasar nan, kamar yadda Vanguard ta rahoto.
A cewarsa:
“Lokacin da suka shigo cikin jama’a, mutane suna gudu amma mutumin da ya yi kama da ‘yan banga ya tsaya yana kokarin yin waya da wani abu kamar wayar walkie talkie. ‘Yan bindigar sun harbe mutumin a ka. Ya fadi ya mutu,
” Ya yi zargin cewa baya ga matar marigayin da ‘yan bindigar suka sace, sun kuma yi garkuwa da wasu mazauna unguwar sama da 10 a wani samame da ya dauki sama da sa'a daya.
Jaridar Punch ta rahoto cewa wasu yan bindiga sun yi garkuwa da Dorcas Vem, matar mataimakin shugaban ma'aikatan gidan gwamnatin Filato, Silas Vem.
Haka nan kuma, a wani harin na daban, yan bindiga sun sace Dakta Samuel Audu, daraktan ma'aikatar lafiya ta jihar Filato.
Majiyoyi daga fadar gwamnatin jihar Filato dake Jos, da kuma hedkwatar ma'aikatar lafiya sun tabbatar da faruwar lamarin ranar Talata.
Legit
Reported by ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye
https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g
Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN
Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN
Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN
Shafukan sada zumunta
Twitter twitter.com/isyakalabari
Facebook facebook.com/isyakalabari