Da duminsa: An damke Lauyan bogi da ya je karban belin wani madamfari, duba yadda ta faru


Hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzkin kasa zagon kasa watau EFCC ta damke lauyan bogi, Adekola Adekeye, kan laifin kirkiran takardun bogi don damfara.

Kakin hukumar EFCC, Wilson Uwujaren ya bayyana hakan a jawabin da ya saki ranar Alhamis a Abuja, rahoton NAN.

Ya ce asirin lauyan ya tonu ne lokacin da yaje ofishin hukumar karban belin wani dan damfara.

A cewarsa:

"A ranar 11 ga Junairu, 2022, ya zo ofishinmu na Legas karban belin wani mutumi da ake yiwa zargin damfara."

"Amma asirin Adekeye ya tonu lokacin da jami'ai suka bincike takardun da ya gabatar don karban belin mutumin."

Sun je har gidansa don bincike

Uwujaren yace jami'an EFCC sun garzaya gidansa don gudanar da bincike kawai sai suka tarar takardun bogi na jami'ar jihar Legas.

"Yayinda aka gudanar da bincike gidansa, an gano takardun bogi na tun shekarar 2005," yace.

"Ya yi ikirarin cewa shine mai ofishin “A.A. Emmanuel & Co. Chambers”, da yake amfani wajen damfara kafin a damkeshi, Za'a gurfanar da shi a kotu."

Legit

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/G83TOEf1MUmDTiYaMTb02g

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN