Yanzu-yanzu: Kwale-kwale ya kife da daliban Islamiyya a jihar Kano, mutum 20 sun mutu, duba sanadi

Kwale-kwale ya kife da Fasinjoji kimanin 47 ciki har da daliban makarantar Madinatu Islamiyya dake karamar hukumar Bagwai ta jihar Kano. Daily Trust ta ruwaito cewa kwale-kwalen ya kife ne a hanyar zuwa Bagwai dake Badau. Rahoton ya kara da cewa daliban na hanyarsu ta zuwa bikin Maulidi ne don murnar ranan haihuwan Manzon Allah (SAW). Wata majiyar ya bayyana cewa sama da fasinjoji 40 wannan abu ya shafa, Majiyar, wacce ke asibitin Bagwai ta bayyana cewa kawo yanzu an gani gawawwaki mutum 20 kuma an ajiyesu a dakin ajiye gawawwaki. Read more: https://hausa.legit.ng/news/1445735-yanzu-yanzu-kwale-kwale-ya-kife-da-daliban-islamiyya-a-jihar-kan Kwale-kwale ya kife da Fasinjoji kimanin 47 ciki har da daliban makarantar Madinatu Islamiyya dake karamar hukumar Bagwai ta jihar Kano. Daily Trust ta ruwaito cewa kwale-kwalen ya kife ne a hanyar zuwa Bagwai dake Badau.Reported by ISYAKU.COM


Kwale-kwale ya kife da Fasinjoji kimanin 47 ciki har da daliban makarantar Madinatu Islamiyya dake karamar hukumar Bagwai ta jihar Kano. Daily Trust ta ruwaito cewa kwale-kwalen ya kife ne a hanyar zuwa Bagwai dake Badau.


Rahoton ya kara da cewa daliban na hanyarsu ta zuwa bikin Maulidi ne don murnar ranan haihuwan Manzon Allah (SAW). Wata majiyar ya bayyana cewa sama da fasinjoji 40 wannan abu ya shafa,


Majiyar, wacce ke asibitin Bagwai ta bayyana cewa kawo yanzu an gani gawawwaki mutum 20 kuma an ajiyesu a dakin ajiye gawawwaki.


An ceto mutum 7, an tabbatar da mutuwar 20 Kakakin hukumar kwana-kwanan jihar Kano, Saminu Abdullahi, ya ce da misalin karfe 9:15 na dare an tura jami'ai kai dauki, Daily Trust ta jiyo. Ya tabbatar da labarin cewa an gano gawawwaki 20. Ya yi karin bayanin cewa kwale-kwalen na dauke da mutum 47

.

Yace: "A yanzu da muke magana jami'an kai dauki sun gano gawawwaki 20 kuma sun an tsinci mutum 7 da rai." Mummunan hatsarin mota ya laƙume rayukan mutum 15 a Jigawa Rundunar yan sandan Nigeria reshen jihar Jigawa ta ce a kalla mutane 15 ne suka riga mu gidan gaskiya sakamakon mummunan hatsarin mota da ya faru a jihar.


Mai magana da yawun yan sandan jihar, Lawan Shiisu, a ranar Litinin a garin Dutse ya ce hatsarin ya faru ne a hanyar Achlafiya zuwa Karnaya, The Nation ta ruwaito.


ASP Shiisu ya ce motoci biyu ne hatsarin ya ritsa da su misalin karfe 5 na yamma a karamar hukumar Yan Kwashi na jihar. Ya ce: "Motoccin biyu sun hadu ne gaba da gaba, sun yi karon ne yayin da daya daga cikinsu ya ke kokarin kaucewa rami a titin.


Source: Legit


Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN