Yan fashi sun wawushe maƙuden kuɗi daga ATM ɗin wani banki , duba ka gani


The Nation ta gano yadda su ka kasa shiga cikin bankin, su ka afka wa ATM din bankin inda su ka cire duk kudaden da ke ciki. 


Wata majiya daga mazauna yankin ta bayyana yadda ‘yan fashin su ka afka bankin da misalin karfe 2 na dare.


Majiya daga jami’an tsaro ta sanar da wakilin The Nation yadda ‘yan fashin su ka isa wurin da yawansu.


Kamar yadda majiyar ta shaida:


“Yan fashi da yawansu sun afka bankin sanye da sutturun ‘yan sanda. Sun daure wani mafarauci da ke gadin bankin yayin da sauran su ka tsere su na neman dauki.

“Kafin ‘yan sanda su isa wurin, har sun balle ATM din bankin sun yashe kudaden da ke ciki. Amma ba su samu damar shiga bankin ba.”

Kakakin rundunar ‘yan sandan yankin, Yemisi Opalola ya tabbatar da aukuwar harin.


A wani labarin, hukumar yaki da rashawa da masu yi wa tattalin arzikin kasa ta'annati, EFCC, ta nemi taimakon 'yan Nigeria wurin neman wasu mutane hudu da ta ayyana nemansu ruwa a jallo kan damfara.


Hukumar a shafinta na Facebook, a ranar Litinin, 22 ga watan Nuwamba ta ayyana neman Akpodemaye Ikolo, Donald Olorunkoyede, Owootomo Tomilola Sunday, da Okuafiaka Bright Onyebuchi ruwa a jallo.


EFCC ta ce ana bincikar wadanda ake zargin ne kan laifuka masu alaka da damfara. Hukumar ta bukaci duk wani da ke da bayani mai amfani dangane da inda mutanen suke ya tuntubi ofisoshinta a kasar.


Majiyoyi da dama sun sanar da Premium Times cewa babu asarar rai ko daya da aka yi sakamakon harin da aka kwashe sa’o’i biyu ana yi.


Har yanzu ba a ji komai ba daga wurin masu garkuwa da mutanen

Bahisulhaq Alhassan, dan uwan basaraken, ya sanar da Premium Times a Katsina cewa a ranar Talata an kwashe sauran iyalan dagacin kauyen daga kauyen.


A cewarsa:


“Har yanzu ba mu ji daga gare su ba (masu garkuwa da mutanen), sai dai mu na fatan ko wasika su turo wa mutane don a san abinda za ayi.”

Habib Daudawa, wani mazaunin yankin da ke jihar Katsina ma ya kara tabbatar da harin.


Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Gambo Isa bai bayar da martani akan sakon da aka tura masa ba, sannan bai yi tsokaci ga sakon WhatsApp din da Premium Times ta tura masa ba.


A wani labarin, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci shugabannin tsaron kasar nan da su kawo karshen ta’addancin da ke aukuwa a kasa musamman a hanyar Abuja zuwa Kaduna.


Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ya sanar da hakan a ranar Alhamis bayan wani taro da shugaban kasa ya yi da kwamitin tsaron kasa, NSC a fadarsa da ke Abuja, Daily Trust ta ruwaito.


A cewarsa shugaban kasan ya ba ‘yan sanda da duk wasu jami’an tsaro ciki har da jami’an binciken sirri umarnin kada su zauna har sai sun kawo karshen ta’addanci, rashin tsaro, amsar kudaden fansa da sauransu a Najeriya.


Source: Legit

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN